Connect with us

News

Daga Karshe Buhari Ya Saki Dariye Da Nyame Daga Kurkuku

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata hudu bayan Gwamnatin Tarayya ta yi wa tsofaffin Gwamnonin jihohin Filato da Taraba, Joshua Dariye da Jolly Nyame, afuwa, daga karshe an sake su daga gidan gyaran hali.

An dai daure su ne tun da farko kan zargin karkatar da biliyoyin kudaden lokacin da suke jan ragamar jihohunsu.

Advertisement

Idan ba a manta ba dai kotun ta yanke wa Nyame daurin shekara 12 sakamakon samunsa da laifin karkatar da Naira biliyan 1.64 lokacin da ya ke Gwamnan jihar Taraba, yayin da Dariye aka yanke masa shekaru 10 sakamakon badakalar Naira Biliyan 1.26.

Wata majiya daga gidan yarin Kuje ta sanar da Aminiya cewa an sako tsoffin Gwamnonin ne da karfe 2:15 na ranar Litinin.

Advertisement

Haka zalika an sako wasu ukun daga gidan yarin Suleja da ke jihar Neja, bisa dalilan rashin lafiya, da tsufa, da kuma nuna kyawawan dabi`u a zamansu a kurkuku a cewar majiyar ta mu.

Duk kokarin da mu ka yi domin jin ta bakin Kakakin gidan yarin Abubakar Umar ya ci tura, sai dai wani jami`i ya tabbatar mana da cewa ya na gudanar da taro ne.

Advertisement

saoi kadan da bayyana wannan hukunci na Gwamnatin tarayya lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin al`umma, in da wasu suke ganin sam bai dace ba.

Daily Trust

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending