Connect with us

News

Ecowas ta dakatar da daukar ma’aikata saboda zargin wariya

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kungiyar raya kasashen yammacin Afirka – ECOWAS ta dakatar da daukar ma’aikata.

Kakakin majalisar dokokin kungiyar, Mr. Sidie Tunis, ne ya bayar da umarnin yana mai cewa matakin zai soma aiki nan take.

Advertisement

An bayar da umarnin ne bayan zargin da tawagar Najeriya ta yi cewa an nuna wa masu neman aiki daga ƙasar wariya a wajen daukar aiki da kuma ƙarin girma.

Masu wakiltar Najeriya a kungiyar ta ECOWAS sun kuma yi barazanar janyewa daga ƙungiyar da kuma daina ba da ƙudade domin raya ƙungiyar.

Advertisement

Sun zargi cewa akwai manyan ma’aikata a kungiyar da ke daukar ‘yan uwansu da mutanen da ransu yake so ba bisa ƙa’ida ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending