Connect with us

News

Ganduje ya aikawa majalisa ƙarin sunan mutum don tantacewa a matsayin Kwamishina

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

 

 

 

Advertisement

 

Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya miƙa ƙarin sunan mutum ɗaya, wani, Ali Musa Burum-burum ga Majalisar Dokokin Kano- domin tantancewa a matsayin Kwamishina.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa a jiya ne dai Ganduje ya aika da sunayen mutane 8 zuwa ga majalisar domin tantancewa a matsayin kwamishinoni don maye guraben waɗanda su ka yi murabus domin tsaya wa takara.

Babban Sakataren yaɗa labaran Majalisar, Uba Abdullahi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

Yace karin sunan na ɗauke ne cikin wata wasiƙa da gwamnan ya aike wa Shugaban majalisar, Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari.

Sanarwar ta ce ana sa ran Ali Musa Burum-burum zai kasance cikin mutane 8 da Majalisar ta bukaci suje majalisar a mako mai zuwa domin tantance wa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending