News
Zan miƙa ragamar jami’o’in gwamnatin tarayya a hannun jihohi idan na ci zaɓe — Atiku
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Ɗan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya lashi takobin mika wa gwamnatocin jihohin kasar dukkan jami’o’in da ke karkashin kulawar gwamantin tarayyar kasar idan aka zabe shi a amatsayin shugaban kasar a shekara mai zuwa.
Atiku na jawabi ne yayin wani babban taro na kungiyar lauyoyin Najeriya da ya gudana a babban birnin kasuwanci na kasar wato Legas.
Jaridar daily Trust ta ruwaito Atikun na cewa kadarorin da Najeriya ta mallaka na iya karewa nan ba da dadewa ba:
“Daya daga cikin abubuwan da na shirya yi shi ne karfafa wa bangaren ‘yan kasuwa – na cikin gida da na waje – da su zuba jari a banagren ilimi domin Najeriya ba ta da kadarorin da za su dade tana sarrafa su kamar yadda take yi a yanzu.”
Ya kuma yi tsokaci kan talaucin da ya addabi yawancin ‘yan kasar, yana cewa “tun bayan da Najeriya ta koma bisa turbar dimokradiyya a 1998/99, kasar ba ta taba samun kanta cikin tasko kamar wanda ta ke ciki ba a yanzu.”
.
Daily Nigerian
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
