News
Asibitin koyarwa na Yobe zai fara aikin dashen ƙoda – Kwamishina
Daga: Hamza Yusuf Abdulmumin
Dakta Mohammed Gana, Kwamishinan Lafiya da Ayyukan Jama’a na Yobe ya ce nan ba da jimawa ba asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar, YSUTH, Damaturu, zai fara aikin dashen ƙoda.
Gana ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN a Damaturu a yau Talat, cewa asibitin zai gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar Cibiyar Urology da Nephrology, na Jami’ar Mansoura ta ƙasar Masar.
Gana ya ce, haɗin gwiwar zai sanya likitocin cibiyar da za su ziyarci YSUTH domin gudanar da aikin dashen koda da kuma likitocin YSUTH da ke samun horo mai zurfi kan ilimin nephrology a cibiyar da ke Masar.
“Babban maganin ciwon koda shine dashen koda kuma mun san tsadar sa da wahalarsa.
“A saboda haka ne Gwamna Mai Mala Buni ya yanke shawarar samar da kayan aikin dashen koda ga YSUTH, tunda asibitin yana da karfin da zai iya amfani da su tare da horo mai kyau.
“Duk wadannan da nufin rage farashin maganin koda da kuma kawo taimako ga mutanenmu,” in ji kwamishinan.
Ya ce wankin ƙoda kyauta ne a asibitin, inda ya ce nan ba da daɗewa ba za a samar da sabbin na’urorin wankin ƙodar na zamani a garuruwan Gashua da Nguru, yankunan da cutar ta fi kamari.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
