News
Gwamna Buni Ya Ba Iyalan Malamin Da Aka Kashe Aiki Yi
Daga: Hamza Yusuf Abdulmumin
Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bayar da aikin yi kai tsaye ga ‘ya’yan marigayi malamin addinin Islama, Sheikh Goni Aisami da aka kashe a ranar Juma’ar da ta gabata a kusa da Gashua, kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.
Gwamna Buni ya ba da umarnin ne a ranar Talata lokacin da ‘yan uwan marigayin suka ziyarce shi domin nuna jin dadinsu kan yadda ya ke nuna damuwarsa ga iyalan.
Gwamna Buni ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Mamman Mohammed ya tabbatar da cewa gwamnati za ta tabbatar da gudanar da bincike kan lamarin mutuwar malamin.
Ya kuma ba da tabbacin gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ‘yan uwan Mamacin domin sun yi asarar rashin Malamin
Malam Ibrahim Aisami, wanda ya yi magana a madadin ‘yan uwa, ya nuna jin dadinsa da sakon ta’aziyya da ziyarar da wata babbar tawagar gwamnati ta kai domin jajantawa iyalan.
Ya ce aikin zai rage wa iyalansu wahala sakamakon rasuwar malamin.
Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, A ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu mutane biyu da ake zargin sojoji ne suka kashe Sheikh Aisami.
A halin da ake ciki, ‘yan sanda sun kama wadanda ake zargin yayin da rundunar sojin ta sanar da cewa ta fara gudanar da bincike a kan lamarin domin bayyana cikakken bayani kuma duk wanda aka samu da hannu a kisan malamin zai fuskanci shari’a.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
