Uncategorized
APC na son amfani da Jonathan – Mai fafutuka
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Mai fafutuka kuma mai kiran ‘yan Najeriya, Deji Adeyanju, ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress na shirin yin amfani da kuma yin watsi da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.
Hakan na zuwa ne biyo bayan ziyarar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya kai wa Jonathan a Abuja, a daren ranar Talata.
Adeyanju ya tunatar da tsohon shugaban kasar irin rawar da ‘yan jam’iyyar APC suka taka a lokacin zaben fidda gwani na takarar shugaban kasa, inda ya ce tun da farko ya gargade shi da yin amfani da shi.
Kotu Ta Daure Mutumin Da Ya Kashe Kaninsa
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Tinubu wanda ya samu rakiyar mataimakinsa Sanata Kashim Shetimma ya jagoranci tawagar gwamnonin APC biyar. Sun hada da gwamnan jihar Filato da kuma babban darakta na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, Simon Lalong; takwaransa na jihar Ogun, Dapo Abiodun; Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawale; Gwamnan jihar Jigawa, Abubakar Badaru da gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman
Duk da cewa ba a bayyana cikakken bayanin taron ba, wata majiya a sansanin Tinubu ta shaida wa wakilinmu cewa ziyarar ta kasance tsawaita tuntubar shugaban jam’iyyar APC na kasa da manyan masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2023.
“Ziyarsa ta Jonathan bai kamata ta ba kowa mamaki ba. Tinubu ba ya zagi da duk wani shugaban siyasa ko a cikin jam’iyya ko a jam’iyyar adawa,” inji majiyar.
Da yake mayar da martani ta shafin Facebook, Adeyanju ya ce, “Ya kai Goodluck Jonathan, ba za ka mutu ba idan ba ka goyon bayan kowa a wannan zaben. A lokacin zabukan fidda gwani na jam’iyyar APC lokacin da ‘yan jam’iyyar ke yaudarar ku, da fatan ku tuna duk gargadin da na yi muku cewa kawai sun so su yi amfani da ku ne su jefar da ku. Magana ta isa ga masu hankali.”
PUNCH
