News
Kotu Ta Daure Mutumin Da Ya Kashe Kaninsa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata kotun majistare da ke Kano ta bada umarnin tsare wani mutum mai shekaru 37 a gidan gyaran hali, bisa yi wa kaninsa duka har sai da ya mutu.
’Yan sanda dai sun kama Jamilu ne da ke zaune a unguwar Chediyar Kuka a Kano, bisa zarginsa da aikata laifin kisan kai.
Kotu Ta Sake Fatali Da Bukatar Bayar Da Belin Abba Kyari
Dan Sanda mai gabatar da kara Aminu Dandago ya sanar da kotun cewa da karfe 10:00 na daren ranar 13 ga watan Fabrairun 2022 ne a unguwar ta Chediyar Kuka, matashin ya rufe kaninsa mai shekaru 30 da duka a sakamakon wani sabani da suka samu.
A cewarsa dukan ya haddasa wa kanin nasa rauni a cikin nasa, har sai da aka kai shi Asibitin na Murtala, in da ya rasu.
Dandago ya ce laifin ya saba wa sashi na 221 na kundin Penal code.
Alkalim kotun dai ya dage karar zuwa ranar 8 ga watan Satumaba 2022.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
