Connect with us

News

Wuta Ta Kona Gine-gine Yayin Da Tankar mai Ta Fashe

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

 

 

 

Kimanin gine-gine 10 ne suka kone kurmus bayan da wata tankar da ke dauke da kaya ta fado kuma ta fashe a kan iyakar Olambe da Matogun da ke karamar hukumar Ifo ta jihar Ogun ranar Asabar.

Advertisement

Ko’odinetan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa Ibrahim Farinloye, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar ya ce ba a samu asarar rayuka ba.

Jam’iyyar ADC a Najeriya ta dakatar da ɗan takararta na shugaban ƙasa

Farinloye ya ce, “Wata tankar mai dauke da kimanin lita 45,000 na PMS ta yi hatsari, ta zubar da abin da ke cikinta sannan ta fashe da misalin karfe 7 na safe a Olambe, kan titin Matogun, a karamar hukumar Ifo, jihar Ogun.

“Duk da cewa babu wani rai da aka rasa ko kuma wani ya samu rauni amma kusan gine-gine 10 ne suka cinye a lamarin.”

A halin yanzu dai an kashe wutar.

 

Advertisement

 

 

 

PUNCH

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending