Connect with us

News

Mutum 8 Sun Nitse A Ruwa A Jigawa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Mutum takwassun rasa rayukansu a sanadiyyar kifewar kwalekwale da kuma nitsewa a ruwa a kananan hukumomin Gwaram da Kaugama da ke jihar Jigawa.

Advertisement

 

Rahotanni sun ce mutum biyar dai sun rasu ne a kauyen Martaba da ke karamar hukumar Gwaram, inda aka sami nasarar ceto hudu daga cikinsu.

Advertisement

 

 

Advertisement

A wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan jihar, DSP Lawan Shi’isu Adam, kwalekwalen ya kife da mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga masallaci.

Yan bindiga sun yi garkuwa da matafiya da dama a jihar Ondo

Advertisement

“Mutane hudu, da suka hada da wani mai shekara 60 mai suna Barkeji, sun tsira da rayukansu inda aka samu ceto su da ransu,” inji Kakakin.

 

Advertisement

Ya kuma ce a sanadiyyar gudunmawar da wasu masunta suka kai, an sami gawawwaki biyar da suka hada da wani dattijo mai suna Lukateru mai shekara 60 da Musa mai shekara 50 da Sale mai shekara 50 da Alhaji Shuaibu mai shekara 60 da Dogo mai shekara 50, dukkansu mazauna garin Darazau da ke Jihar Bauchi.

 

Advertisement

Ya kara da cewa, tuni an mika gawawwakin ga iyalai da yan uwan su domin yi musu jana’iza.

 

Advertisement

A wani labarin kuma, wasu yara mata uku, sun rasu a sakamakon nitsewa a ruwa a kauyen Faskarau da ke garin Ja’e a karamar hukumar Kaugaman ta jihar Jigawan.

 

Advertisement

Yaran sun hada da Maryam Salisu mai shekara 10 da Bahayura Lawan, ita mai shekara 10 da kuma Lawisa Sule mai shekara takwas a duniya.

 

Advertisement

A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar tsaro ta NSCDC, CSC Adamu Shehu, ya fitar ranar Litinin, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:00 na safiyar Litinin, yayin da suka je wanki a rafi.

 

Advertisement

Ya ce an kai gawarwakinsu babban asibitin Kaugama, inda likita ya tabbatar da rasuwarsu.

 

Advertisement

Bincike ya nuna cewar, yaran, bayan sun gama wankin nasu ne suka yanke shawarar yin wanka, lamarin da ya jawo rasa rayukansu.

 

Advertisement

Mazauna yankin sun tabbatar da cewar shekaru 20 da suka gabata, an taba samun irin wannan iftila’in inda yara uku mata suka rasu.

 

Advertisement

Tuni aka yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada bayan mika gawarwakinsu ga iyalansu.

 

Advertisement

A nasa bangaren, babban kwamandan rundunar ta NSCDC a jihar, Musa Alhaji Mala ya jajanta wa iyalan mamatan, gami da jan hankalin iyaye da su kula wajen tura yara rafi, musamman a wannan lokacin da ake fama da ambaliyar ruwa a fadin Jihar.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending