News
Yan Sanda Sun Yi Gumurzu da Yan Bindiga, Sun Ceto Dan Takarar PDP a Katsina.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Dakarun rundunar ‘yan sanda reshen jihar Katsina, sun kuɓutar da ɗan takarar majalisar jiha mai wakiltar Kankiya a inuwar PDP, Ibrahim Tafashiya, daga hannun ‘yan ta’adda.
Rahotanni sun ce tun da farko a daren ranar asabar, ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da Tafashiya a yankin ƙaramar hukumar Kankiya.
APC: Machina ya musanta janyewa daga takarar Sanatan Yobe ta Arewa
Bayan sanar da ‘yan sanda lamarin garkuwan, nan take DPO na caji Ofis ɗin Kankiya, SP Iliyasu Ibrahim da ‘yan tawagarsa suka toshe hanyar fitar maharan, suka yi ɗauki-ba-daɗi da su har suka samu nasarar ceto ɗan takarar.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da wannan nasara a jiya Lahadi.
Wasu rahotanni sun nuna cewa ‘yan ta’adda sun shiga gidan Rijistaran kwalejin ilimi ta tuna wa da Isah Kaita (IKCOE), Salisu Gide, dake cikin garin Kankiya, inda suka sace shi da matarsa.
Dakarun ‘yan sandan sun yi nasarar ceto Giɗe, yayin da suke cigaba da kokarin ceto matarsa da sauran mutanen da maharan suka tattara a harin. Kakakin ‘yan sanda ya ƙara da bayanin cewa an ga ‘yan ta’adda a wani wuri dake yankin ƙaramar hukumar Batsari, cikin jihar Katsina.
Sannu a hankali dai hare haren ƴan bindiga na ƙarasowa garin na Kankiya, wanda ke kan hanyar Kano zuwa Katsina.
Mutane da dama mazauna ƙauyukan da ke ƙaramar hukumar Kurfi sun tsere daga gidajen su, sun dawo garin na Kankiya.
Masana harkokin tsaro sun yi gargadin cewa, idan har hare haren ƴan bindiga ya ɗore a garin na Kankiya, toh lallai zai yi barazana ga dubban matafiyan da sintiri daga Kano zuwa birnin Katsina.
LIBERTY NEWS
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
