An tsaurara matakan tsaro a wannan Litinin din a Kenya, yayinda ake sa ran kotun koli ta yanke hukunci kan kalubalantar sakamakon zaben shugabancin kasar da aka shigar a gabanta.
Hukumar zabe ta kasar ta bayyana mataimakin shugaban kasa, William Ruto a matsayin wanda ya yi nasara.
Davido ya lashe Kyauta mafi kyawun ɗan adam, Digital Artiste Awards
Sai dai abokin hamayyarsa, Raila Odinga, ya zargi cewa an yi aringizon kuri’u. Wakiliyar BBC ta ce, Odinga na son Kotu ta soke sakamakon ko kuma ta sanar da shi a matsayin wanda ya lashe zaben ko kuma ta umarci a sake gudanar da wani zabe.
Mista Ruto dai ya yi watsi da zarge-zarge Odinga. Mutanen biyu sun ce zasu rungumi hukunci da kotun koli za ta yanke.
