Connect with us

News

Yan Sanda Sun Yi Ram Da Wani Likita Kan Mutuwar Direban

Published

on

Police

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo tayi hulin wani likita bisa mutuwar wani direban taksi a garin Benin babban birnin jihar.

Wanda ake zargin, Dokta Abass Adeyemi wanda ya fito daga karamar hukumar Offa ta jihar Kwara ana zarginsa da kashe direban taksin a ranar 3 ga watan Satumba, 2022, a cikin garin Benin tare da jefar da gawarsa a unguwar Otofure, bayan Oluku a karamar hukumar Ovia ta Arewa maso Gabas.

Advertisement

Saudiyya na son daukar nauyin bikin baje-koli na 2030

Yayin da yake gabatar da wanda ake zargin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Edo, Chidi Nwabuzor, ya ce Abass Adeyemi ya gana da mamacin, direban taksin dan asalin jihar Delta Emmanuel Agbovinuere a cikin garin Benin a cikin watan Yulin wannan shekarar a lokacin da yake gudanar da aikinsa.

Advertisement

A cewar Nwabuzor, daga baya sun zama abokan juna wanda shine dalilin da ya sa marigayin ya sake amsa gayyatar wanda ake zargin a ranar uku ga watan Satumba a lokacin da ya isa Benin domin yin sana’ar sa ta haya da motarsa.

Ya ce wannan shi ne karo na karshe da aka ga direban taksin da rai.

Advertisement

Wanda ake zargin wanda ya ki amsa tambayoyin ‘yan jarida, ya roki iyalan marigayin da suyi masa gafara.

Rundunar ‘yan sandan ta ce za a gudanar da cikakken bincike daga bisani za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Alkibila

 

Advertisement

 

.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending