News
Wutar lantarki ta fara dawo wa a faɗin Nijeriya — TCN
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kasa (TCN) ya ce an fara aikin gyaran layin wutar ƙasa da ya sauka gaba ɗaya a faɗin ƙasar nan a safiyar yau Litinin din nan.
“An fara dawo da sashin layin da abin ya shafa kai tsaye da karfe 11.55 na safe, inda Osogbo da Ihovbor suka koma kan layi.
” sai Jebba da Osogbo, Kainji da Jebba, Benin da Onisha, Shiroro da Kaduna, Shiroro da Katampe, da Alaoji da Ikot. Ekpene, ”in ji shi a cikin wata sanarwa a ranar Litinin.
“Sauran sun hada da Lokoja da Gwagwalada, Odukpani da Ikot Ekpene, Benin da Omotosho, Oke-Aro da Ikeja west, Egbin da Oke-Aro and Kaduna da Kano.” in ji sanarwar
Advertisements
