News
Shugaban matasan PDP na kasa, Kadade ya shiga cikin fitattun mutane 100 a duniya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wata kungiyar kwararru da ke kula da shugabanni masu tasiri a duniya, MIPAD, ƙarƙashin kulawar zauren majalisar dinkin duniya, ta zabi Hon. Muhammad Kadade Suleiman, Shugaban Matasa na PDP na Ƙasa a matsayin ɗaya daga cikin fitattun mutane guda dari mafiya tasiri a shekarar 2022.
MIPAD ta aike wa da uwar jam’iyyar PDP, ta na mai sanar da ita zaɓen Kadade a matsayin ɗaya daga cikin fitattun mutane dari mafiya tasiri a shekarar 2022.
NDLEA ta kama ƙwayoyin Tramadol guda miliyan 13 a Legas
Shugaban matasan PDP na kasa Kadade na ɗaya daga cikin ƴan kwamatin zartaswar jam’iyyar PDP da aka zaɓa a shekarar da ta gabata a yayin babban taron jam’iyyar da ta zabi sabbin shugabanni.
Kasancewar shugaban matasan PDP na kasa, Kadade matashi ɗan shekaru 26, ya sanya zabensa ya ja hankali a ciki da wajen Najeriya.
Shi ne na farko mai karancin shekaru da ya taɓa rike irin wannan mukamin a tarihin jamiyyun siyasa a Najeriya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
