News
Trump ya maka gidan talabijin na CNN kotu
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya maka gidan Talabijin na CNN kotu bisa zargin bata masa suna.
Trump ya zargi sanannen gidan talabijin din na Amurka da bata masa suna, inda yace sun kwatanta shi da Adolf Hitler na Jamus.
Yayin da ASUU ke yajin aiki:Shugaba kasa muhammadu Buhari na shirin karrama ministan Ilimi.
Akan haka tsohon Shugaban Amurkar ya nemi diyyar dala miliyan ɗari huɗu da saba’in da biyar.
Donald Trump ya shigar da kara mai shafi 29 a wata kotu da ke Florida, inda yake zargin CNN da ƙoƙarin yi masa maƙarƙashiya.
To amma zuwa yanzu gidan talabijin na CNN din bai mayar da martani ba.
Advertisements
