News
ASUU za ta kai karar gwamnati kan rijistar sabbin kungiyoyin malaman jami’o’i biyu .
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU za ta kai karar gwamnatin kasar kan rijistar da ta yi wa sabbin kungiyoyi na malaman wato CONUA da NAMDA ( Congress of Nigerian Universities Academics, da National Association of Medical and Dental Academics)
Lauyan kungiyar ta ASUU, Femi Falana, shi ne ya bayyana haka a wata hira ta tashar talabijin ta Channels Television, a yau Alhamis, inda ya ce za su kalubalanci yi wa kungiyoyin biyu rijistar.
Dan Wasan Chess Da Ake Zargi Da Magudi Ya Yi Biris Da Martanin Mutane
A ranar Talata ne ministan kwadago, Chris Ngige, ya bayar da takardar shedar rijista ga sabbin kungiyoyin biyu da ke zaman kamar kishiyoyi ga ASUU.
A lokacin da yake ba su takardar Ngige, ya ce kungiyoyin biyu za su wanzu kafada da kafada da ASUU>
Ita dai ASUU tana yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu, inda mambobinta wato malaman jami’o’in gwamnati suka dakatar da aiki a kan kin biyansu kudaden alawus-alawus tare da neman kyautata jin dadinsu da sauran bukatu daga gwamnatin tarayya.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
