Connect with us

News

Likita ta shawarci ƴan Nijeriya da su rika samun isasshen hutu da guje wa yawan yin aiki

Published

on

Yashua Alkali-Hamza

 

DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAH

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

Wata likitar yara da lafiyar al’umma a Abuja, Dakta Yashua Alkali-Hamza, ta gargaɗi ƴan Nijeriya da su kiyaye daga salon rayuwa na yin aiki tuƙuru ba tare da hutawa ba.

Ta tabbatar da cewa ƴan Nijeriya za su samu koshin lafiya idan sun saba da al’adar huta wa.

Alkali-Hamza, wadda ita ce babbar jami’a a asibitin kula da kananan yara da jin dadin jama’a, ta bayyana cewa hutu na kara karfin garkuwar jiki da ake bukata domin kawar da cututtuka masu barazana ga rayuwa.

Advertisement

“samin hutu da kuma kwantar da hankali na da mahimmanci ga kowane ɗan adam. Abin da mutane da yawa ba su fahimta ba shine yawancin cututtukan mu su na faruwa ne ta hanyar rashin samun hutu.

“Ba kawai hawan jini ko cututtukan zuciya ba, har ma da waɗanda ake ganin suna haifar da su ta hanyar ƙwayoyin cuta, cututtukan da rashin ƙarfin garkuwar jiki ke haifar wa da sauran cututtuka na yau da kullum.

“Wannan shi ne saboda damuwa na hana jikinmu ya kasance cikin daidaito. Dukanmu mu na da garkuwar jiki da ke bamu kariya da ga shigar cututtuka.

” Lokacin da muke cikin ranshin hutu, wannan tsarin garkuwar jikin na rushewa. Shi ya sa mutane biyu za su iya fuskantar abu ɗaya amma sai ka ga ɗaya ya kamu dayan kuma bai kamu ba,” in ji ta.

 

 

Advertisement

 

Daily Nigerian

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending