News
2023: Za Mu Hana Baki Yin Zabe A Najeriya —Imigireshan
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, ta kuduri aniyar hana wadanda ba ‘yan Nijeriya ba kada kuri’a a zaben shekara ta 2023, tare da alkawarin tabbatar da ganin an yi zabubbuka cikin gaskiya da sahihanci.
Mataimakin Kwanturola-Janar mai kula da shiyya ta uku ACG Isma’ila Abba Aliyu ya sanar da haka a Damaturu na Jihar Yobe, inda ya ce Hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen hana wadanda ba ‘yan Nijeriya shiga zabe ba.
Ba mu da shirin tayar da hatsaniya a zaben 2023 – IPOB
Ya ce ko a lokacin yakin neman zabe, jami’an su za su sa ido domin tabbatar da ganin baki ba su shiga cikin harkokin siyasa ba, saboda wannan ya na daya daga cikin lokuta masu mahimmanci.
Isma’ila Abba Aliyu, ya ce za su kuma yi amfani da na’urorin zamani domin sa ido a kan motsin mutanen da ake shakku a kan su, kuma dole ne su yi bayanin kowa domin kauce wa yin barna da sunan Nijeriya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
