News
Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
Gwamnatin Tarayya ta fara raba tan 12,000 na kayan abinci da wasu kayan da ba na abinci ba a jihohin da ambaliyar ruwa ta addabe su.
A ranar Juma’a aka kai wa Jihar Anambra wasu kayan da ba na abinci ba irin su tabarmin roba 7,350, gidan sauro 1,000, katan 600 na sabulun wanka, yadikan shadda 2,500 (kowanne yadi 5), sababbin tufafi na yara guda 1,000, sababbin tufafi na mata 1,000, da sababbin tufafi na maza 1,000.
Mun Warware Kararraki 586 Cikin Sama Da 604 Da Aka Samu A Kwara – Hukumar Korafe-korafe
Haka kuma za a kai wa jihar kayan abinci da su ka haɗa da buhun shinkafa 1,400, buhun wake 1,400 mai awon kilo 10, buhun masara 1,400 mai awon kilo 10, buhun gishiri 75 (awon kilo 20), jarkar man girki 75 (awon lita 20), katan 100 na magi da sauran su, da katan 75 na tumatirin kwali (sacat 50 cikin kowane katan).
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta bayyana wannan hoɓɓasan a jawabin ta a taron Ranar Rage Aukuwar Bala’o’i ta Duniya ta bana (2022 International Day for Disaster Risk Reduction) wanda aka yi a Abuja a ranar Juma’a.
Ministar, wadda ta samu wakilcin Daraktan Harkokin Agaji a ma’aikatar ta, Alhaji Ali Grema, ta ce ana ƙoƙarin a ƙara azama wajen tunkarar matsalolin ambaliya a ƙasar nan.
Ta ce: “Duk dai ku na sane da ambaliya mai yawan gaske ta ke ta ragargazar jihohi da ƙananan hukumomi da garuruwa da dama a Nijeriya. Girman ɓarnar wannan ambaliya a ƙasar nan za a iya kwatanta shi ne kawai da ambaliyar da ta auku a cikin shekarar 2012.
“An yi asarar rayukan sama da mutum 500, kuma sama da mutum miliyan 1.4 abin ya shafa, kimanin gidaje 90,000 sun ruguje ko sashen su ya lalace, kuma bala’in na ci gaba.
Ministar ta bayyana cewa ma’aikatar ta da dukkan masu ruwa da tsaki su na nan su na aikin aiwatar da Tsarin Agajin Gaggawa Ga Ambaliya na Ƙasa (National Flood Emergency Preparedness and Response Plan) wanda Majalisar Gudanarwa ta Tarayya ta amince da shi kwanan nan.
Hajiya Sadiya ta ce: “Tsarin ya gindaya wa dukkan jihohi da ƙananan hukumomi da ma gidaje da garuruwa da ƙungiyoyin sa ido ainihin aiki da kuma haƙƙin da ya rataya a wuyan kowannen su.
A wata hira da aka yi da shi, Darakta-Janar na Hukumar Agajin Gaggawa (NEMA), Mustapha Habib Ahmed, shi ma ya ba da tabbacin cewa an fara raba kayan agaji a sauran jihohi domin a rage wa mutanen da bala’in ambaliya ya shafa a jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya.
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News4 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News21 hours ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
