Connect with us

News

Matawalle Ya Nemi Afuwar Kafofin Yada Labaran Da Ya Rufe

Published

on

Gwamnan Zamfara, Bello Muhammad Matawalle

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

Gwamnatin Zamfara ta ba da hakuri kan matakin rufe wasu kafafen yada labarai a jihar, wanda ya ja mata Allah wadai.

 

Kafofin yada labaran da lamarin ya shafa sun hada da tashar NTA da gidan Pride FM da ke Gusau, baki dayansu mallakar mallakin Gwamnatin Tarayya.

Yan wasa 10 a Real Madrid sun lashe Ballon d’Or

Advertisement

 

Sai kuma tashar Gamji TV da Gamji FM da Al-umma TV wadanda suke masu zaman kansu.

 

Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai na jihar, Ibrahim Dosara, ya fitar, ta nuna kafofin da aka rufen sun saba wa dokar jihar da ma ta aikin jarida, shi ya sa aka dauki matakin a kansu.

 

A ranar Litinin aka ga jigo a gwamnatin jihar, Dokta Abdullahi Shinkafi, ya mika wa tashoshin da lamarin ya shafa takardar ban-hakuri a madadin gwamnati, a lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi a Gusau.

Advertisement

 

Dokar da gwamnatin ta ce an take, ita ce wadda ta haramta tarurrukan siyasa a jihar saboda dalilai na tsaro.

 

 

 

 

Advertisement

AMINIYA

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending