News
Zan kammala aikin wutar mambilla idan na zama shugaban kasa – Tinubu
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin shawo kan matsaloli da ke arewacin Najeriya ke fuskanta da kuma kasar baki daya muddin ya zama shugaban kasa.
Bola Tinubu ya bayyana hakan ne yayin magana a wani taro da kungiyoyi masu fada aji na arewacin Najeriya da suka hada da kungiyar dattawan arewa da kuma Arewa Consultative Forum suka shiryawa ‘yan takarar shugaban kasa a Arewa House, a JIhar Kaduna.
Darajar Naira Ta Karu A Kasuwar Canjin Kudi
Tinubu ya ce cikin abubuwan da zai fara yi shine kammala aikin wutar mambilla da aka shafe tsawon shekaru ba tare da yin aikin ba, inda ya ce tashar za ta samar wa da kasar wuta mai karfin megawatt 3,050 da kuma zai kasance daya daga cikin tasha mafi girma a fadin kasar.
“Abin da yake kawo jinkirin kammala wannan aikin shine rashin isassun kudade. Ba mu iya kebe isassun kudade wa manyan ayyuka masu daukar dogon lokaci. Za mu kammala wadannan ayyuka saboda muna zuwa da wani tsari mai kyau ga kasar,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce zai kawo masu zuba jari a ciki da kuma wajen kasar wadanda za su kammala aikin da kuma zai kawo wa kasar ci gaba.
Bola Tinubu Facebook
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
