Entertainment
Kotu Ta Sa Ranar Yanke Hukunci Kan Karar Da Aka Shigar Da Hadiza Gabon
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Magajin Gari, a Jihar Kaduna ta sa ranar 15 ga watan Nuwamban 2022 don zartar da hukunci a karar da aka shigar da fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon.
Aminiya ta rawaito wani Bala Musa, ma’aikacin gwamnati ya kai karar jarumar bisa zargin kin aurensa bayan ya kashe mata kudin da suka kai har Naira dubu 396.
NDLEA ta kama mutum 130 kan miyagun kwayoyi a jihar Kaduna
Bala dai ya ce sun yi soyayya da jarumar kuma ta yi alkawarin aurensa.
Gabon dai ta musanta saninsa, inda ta ce ba ta taba haduwa da shi ba a rayuwarta.
A ranar Laraba ce Alkalin kotun, Mai Shari’a Malam Rilwanu Kyaudai, ya dage sauraren karar bayan wani babban lauya, Sulaiman Lere, ya roki kotu da ta ba shi dama ya tattauna da bangarorin biyu domin sasanta lamarin.
Lauyan wanda ya shigar da karar, Barista Nurudeen Murtala, ya goyi bayan shawarar sasantawa da Barista Lere ya yi, inda ya kara da cewa sulhu abu ne da Allah yake so, don haka ba za a yi adawa da shi ba.
A nasa bangaren, lauyan wanda ake tuhuma Barista Mubarak Sani, ya goyi bayan shawarar sasantawa amma ya roki kotun da ta saurari shaidun da ya gabatar kan wanda ya shigar da karar.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
