News
Tsohon Alkalin Babban Kotun Kano, Mai Shari’a Wada Umar Rano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 75
Tsohon alkalin Babban Kotun Jihar Kano, Mai Shari’a Wada Umar Rano, ya rasu yana da shekaru 75 a duniya, bayan fama da jinya mai tsawo.
Marigayin ya rasu ne da safiyar yau Alhamis a wani asibiti da ke cikin birnin Kano. Ya yi ritaya daga aikin shari’a a shekarar 2014, bayan shekaru da dama na hidimar gaskiya da rikon amana a cikin kotunan jihar Kano.
Mai Shari’a Rano ya shahara da jajircewa da kishin gaskiya, inda ya taka rawar gani a fagen shari’a da kuma hidimar jama’a. Daya daga cikin muhimman ayyukansa na ƙarshe shi ne jagorantar Kwamitin Binciken Batan Yara a jihar Kano – lamari da ya jawo hankalin al’umma a lokacin mulkin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.
Ya bar mata biyu, da ‘ya’ya da jikoki da dama.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
