News
Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Dakarun shirin sharan daji da ake kira FOREST SANITY sun ce sun yi artabu da ƴan bindiga a yankin Danmarke na ƙaramar hukumar Gummi ta jihar Zamfara lokacin da suke sintiri a yankin.
Sanarwar da sojojin Najeriyar suka fitar a ranar Alhamis ta ce a lokacin artabun ƴan bindigan sun tsere suka bar maɓuyarsu da makamai, yayin da da dama daga cikin su suka samu raunin harbin bindiga.
Dakarun sun samu nasarar kuɓutar da mutum uku, da ƙwato bindigogi ƙirar AK47 guda biyar, da kuma babura 30.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
