Connect with us

News

Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dakarun shirin sharan daji da ake kira FOREST SANITY sun ce sun yi artabu da ƴan bindiga a yankin Danmarke na ƙaramar hukumar Gummi ta jihar Zamfara lokacin da suke sintiri a yankin.

Advertisement

 

Sanarwar da sojojin Najeriyar suka fitar a ranar Alhamis ta ce a lokacin artabun ƴan bindigan sun tsere suka bar maɓuyarsu da makamai, yayin da da dama daga cikin su suka samu raunin harbin bindiga.

Advertisement

 

Dakarun sun samu nasarar kuɓutar da mutum uku, da ƙwato bindigogi ƙirar AK47 guda biyar, da kuma babura 30.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending