Connect with us

News

Mai jego ta kashe jaririnta ta hanyar caka masa wuka bayan da kakar jaririn ta bada shawarar hakan

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wata Matashiya ta kashe jaririn da ta haifa, ta hanyar caka ma Jaririn wuka wanda sanadiyar hakan jaririn ya rasa ransa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Rahotanni sun ce, mahaifiyar matan kuma kakar jaririn, ita ce ta dauki wuka da kanta, ta bai wa ‘yartata’ sannan ta umarceta da ta kashe jaririn saboda kawai yarinyar tayi cikin shege.

Advertisement

 

Wannan lamari dai ya faru ne a garin Olocha-Adogba dake yankin karamar hukumar Awgu dake jihar Enugu a ranar bakwai ga watan da muke ciki na Nuwamba.

Advertisement

2023: Ba Gudu Babu Ja Da Baya Kan Bada Sakamakon Zabe Ta Yanar Gizo – INEC

Gaskiya Ta Fi Kwabo ta jiyo cewa, mahaifiyar Jaririn wato Ada Joy Okonkwo mai shekaru 18, ta haifi jaririn ne sakamakon cikin shege da tayi, wannan shi ya fusata mahaifiyarta mai suna Christiana Okonkwo, ‘yar shekara 60, inda ta dauko wuka da hannunta ta bata sannan ta ce ta kashe jaririn da ta haifa.

Advertisement

Yanzu dai mai jegon da tayi wannan danyen aiki da kuma mahaifiyar ta da ta sanyata ta aikata suna hannun ‘yan sanda.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending