News
Mai jego ta kashe jaririnta ta hanyar caka masa wuka bayan da kakar jaririn ta bada shawarar hakan
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata Matashiya ta kashe jaririn da ta haifa, ta hanyar caka ma Jaririn wuka wanda sanadiyar hakan jaririn ya rasa ransa.
Rahotanni sun ce, mahaifiyar matan kuma kakar jaririn, ita ce ta dauki wuka da kanta, ta bai wa ‘yartata’ sannan ta umarceta da ta kashe jaririn saboda kawai yarinyar tayi cikin shege.
Wannan lamari dai ya faru ne a garin Olocha-Adogba dake yankin karamar hukumar Awgu dake jihar Enugu a ranar bakwai ga watan da muke ciki na Nuwamba.
2023: Ba Gudu Babu Ja Da Baya Kan Bada Sakamakon Zabe Ta Yanar Gizo – INEC
Gaskiya Ta Fi Kwabo ta jiyo cewa, mahaifiyar Jaririn wato Ada Joy Okonkwo mai shekaru 18, ta haifi jaririn ne sakamakon cikin shege da tayi, wannan shi ya fusata mahaifiyarta mai suna Christiana Okonkwo, ‘yar shekara 60, inda ta dauko wuka da hannunta ta bata sannan ta ce ta kashe jaririn da ta haifa.
Yanzu dai mai jegon da tayi wannan danyen aiki da kuma mahaifiyar ta da ta sanyata ta aikata suna hannun ‘yan sanda.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
