News
2023: Ba Gudu Babu Ja Da Baya Kan Bada Sakamakon Zabe Ta Yanar Gizo – INEC
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta yi watsi da ikirarin cewa ta na shirin yin watsi da watsa sakamakon zabe ta yanar gizo (PUs) tare da sauyawa zuwa tashar hukumar INEC wajen sanar da sakamakon zabe (IReV).
Daily trust ta rawaito cewa Kwamishinan na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a Abuja.
ASUU: Sanata Ndume ya ba da shawarar a zabtare albashin ‘yan majalisa a biya malaman Jami’a
A cewarsa, rahotannin da aka samu a wani sashe na kafafen yada labarai cewa INEC na son yin magudi a babban zaben 2023 ta hanyar yin watsi da shigar da sakamakon PUs kai tsaye da kuma na zahiri zuwa tashar IReV ta Registration Area Technical Support Staff (RATECHSS) wato rijistar ma’aikata don tallafin fasaha karya ne a zahiri.
“Hukumar ta sha tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa za ta mika sakamakon zabe kai tsaye daga rumfunan zabe kamar yadda muka shaida a zabukan gwamnonin jihohin Ekiti da Osun da kuma wasu mazabu 103 da aka gudanar da zabukan gwamnoni da na kananan hukumomin birnin tarayya FCT da na kananan hukumomi tun watan Agustan 2020. Har yanzu ana iya duba sakamakon akan shafin.
“IReV na daya daga cikin sabbin abubuwan da Hukumar ta bullo da su don tabbatar da gaskiya da amincin sakamakon zabe a Najeriya. Don haka ba za a yi la’akari da cewa Hukumar za ta juya baya ta yi wa nata abubuwan kirkire-kirkire ba.
“An shawarci jama’a da su yi watsi da rahotannin. Na’urar tantamce sakamakon zabe (BVAS) da IReV sun zo ne don tabbatar da masu jefa ƙuri’a da kuma shigar da sakamakon zabe tun a rumfunan zaɓe a ainihin lokacin a Najeriya, “in ji Okoye.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
