News
INEC ta yi gargaɗi kan tashe-tashen hankula gabanin zaɓen 2023
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya, Mahmood Yakubu ya ce yana fargaba game da ƙaruwar kai hare-hare yayin da ƙasar ke shirya wa babban zaɓen ƙasar a watan Fabrairu mai zuwa.
Ana dai fargaba game da yiwuwar samun tashin-tashina a zaɓen na baɗi wanda ake ganin zai yi zafi.
Barazanar Kotu: Madagwal Ya Ba Sarkin Waka Hakuri
Yakubu ya ce hukumar zaɓen ta gano cewa an samu hare-hare 50 masu alaƙa da zaɓen a cikin watan farko na fara yaƙin neman zaɓe.
Shugaban na INEC ya bayyana hakan ne a wani taron gaggawa da hukumar ta kira bayan kai wa ofisoshinta biyu farmaki.
A Najeriya dai gwamnati na ci gaba da yunƙurin ganin sun magance matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar, waɗanda suka haɗa da na masu iƙirarin jihadi da kuma na ƴan bindiga masu garkuwa da mutane.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
