News
Yan sanda sun gano gida sayar da jarirai a Nasarawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Rundunar ‘yan sanda Nasarawa da ke Najeriya ta ce ta gano gidan da ake zargin sayar da jarirai a karamar hukumar Karu na jihar.
Rundunar ta ce ta ceto mata shida da kuma jariri ɗan wata shida a gidan.
A sanarwar da suka fitar, jami’in hulda da jama’a na yansanda yankin, DSP Ramhan Nansel ya ce da misalin 2 na rana suka kai samame Karu bayan samun wasu bayanan sirri.
Ya ce ana basaja da gidan ne a matsayin gidan kula da marayu. Sai dai bincike ya gano cewa ana garkuwa da kananan yara ana yi musu ciki sannan a sayar da jariran da suka haifa.
An dai cafke wasu mutum uku da ake zargin ke aikata wannan muggun aika-aika.
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
