News
Gobara ta kashe mutum 10 sakamakon dokar kullen korona
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hotunan bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda sabuwar zanga-zangar adawa da kullen korona ta ɓarke a birnin Urumqi na ƙasar China.
Zanga-zangar ta ɓarke ne bayan da wata gobara da ta tashi a wani gini ranar Alhamsi ta kashe mutum 10 a birnin.
Za’a cigaba da fuskantar wahalar man fetur har zuwa sabuwar shekara.
An ga masu zanga-zangar na fuskantar jami’an tsaro, yayin da suke karya shingayen da aka kafa tare da ihun ”a kawo ƙarshen kullen korona”.
To sai dai hukumomin birnin na Urumqi sun musanta zargin cewa dokar kullen ce ta hana mutanen kuɓucewa gobarar.
Birnin wanda ke yammacin ƙasar na cikin dokar kullen korona tun farkon watan Agusta.
Advertisements
