Connect with us

News

A’isha Buhari: Dole ne a saki Aminu – Amnesty

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta ce ya zama wajibi ga hukumomin Najeriya su saki matashin nan da ake zargi da cin mutuncin uwargidar shugaban ƙasar Muhammadu Buhari tare da yin watsi da duk zarge-zargen da ake yi masa.

Advertisement

 

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce ta samu rahotannin da ke cewa an azabtar da matashin bayan kama shi.

Advertisement

Wata mata ta fille kan danta dan wata 11

Ta ce “babban abin kunya ne a ce hukumomin Najeriya sun kama tare da azabtar da Aminu Adamu kawai saboda ya wallafa bayanai a shafin tuwita wanda ya shafi uwargidar shugaban ƙasar.”

 

Advertisement

Bayanin ya ƙara da cewa wannan lamari karan-tsaye ne ga ƴancin bil’adama.

 

Advertisement

Haka nan hukumar ta ce abin da ya kamata hukumomin ƙasar su mayar da hankali a kai shi ne tsarewar da aka yi wa matashin ba bisa ƙa’ida ba da kuma azabtar da shi da aka yi.

 

Advertisement

Bayanai dai sun tabbatar da cewa kotu ta tura matashin mai suna Aminu gidan gyara hali, bayan da aka gurfanar da shi bisa zargin sa da cin mutuncin mai-ɗakin shugaban ƙasa, A’isha Buhari a shafinsa na tuwita.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending