Connect with us

News

Wani dan majalisar dokokin Senegal ya doki takwararsa a zauren majalisa

Published

on

Massata Samb

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

An samu yamutsi a zauren majalisar dokokin Senegal ranar Alhamis bayan wani dan majalisa ya doki takwararsa a ka a yayin da ake nuna zaman majalisar kai-tsaye a talabijin.

 

Advertisement

An fuskanci tsaiko a zaman majalisar lokacin da ake gabatar da kasafin kudi, bayan dan majalisar dokoki daga jam’iyyar hamayya Massata Samb ya bar dandamali inda ya tafi wurin ‘yar majalisa Amy Ndiaye Gniby ta jam’iyyar Benno Bokk Yakaar mai mulki sannan ya doke ta a ka.

Tsohon shugaban jami’ar Gusau zai sha ɗaurin shekara 35

Da take mayar da martani, Ms Gniby ta jefi Mr Samb da kujera, kafin wasu ‘yan majalisar su sanya baki, amma rikicin bai tsaya ba domin kuwa sun yi ta nuashin juna, lamarin da ya sa aka soke zaman majalisar.

Advertisement

 

Kafofin watsa labaran kasar sun rawaito cewa Mr Samb ya tuna wa zauren majalisar wasu kamalai da Ms Gniby ta yi tun da farko wadanda ya ce na “rashin da’a ne”.

Advertisement

 

Daga nan ne Ms Gniby ta mayar da martani daga kujerarta inda ta ce ba ta “damu” ba.

Advertisement

 

Nan take Mr Samb ya daina magana ya ruga a guje inda take.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending