News
Mutum shida sun mutu a haɗarin mota a Kogi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar kiyaye haɗura ta jihar Kogi, ta tabbatar da mutuwar mutum shida yayin da wasu 25 suka samu raunuka a haɗarin mota kan hanyar Okene-Ogori da ke jihar Kogi yau Asabar.
Babban kwamandan hukumar, mista Stephen Dawulung, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN a Lokoja cewa haɗarin ya faru ne lokacin da wata mota dauke da mutane 45 da kuma wasu shanu.
An kama mai shekara 75 da zargin yi wa mai shekara huɗu fyaɗe a Jihar Nasarawa
Kwamandan ya ce haɗarin wanda ya faru da misalin 12 na rana, ya yi sanadiyar mutuwar wasu daga cikin shanun.
Ya kara da cewa bayan faruwar lamarin, ya aike da jami’ansa zuwa wurin, inda a halinn aka tafi da wadanda suka samu raunuka zuwa asibiti domin yi musu magani yayin da aka girke gawarwakin wadanda suka rasu a mutuware da ke garin na Okene.
Babban kwamandan ya yi kira ga direbobi da su kasance masu bin dokokin hanya a kodayaushe domin afkuwar haɗari da tsira da rayukansu.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
