Sports
Benzema ya sanar da kawo karshen bugawa Faransa wasa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Karim Benzema ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon kafa a kasa da sa’o’i 24 bayan da Faransa ta sha kashi a hannun Argentina a wasan karshe na cin kofin duniya na 2022.
Benzema yana cikin tawagar Faransa domin buga wasa a Qatar amma ya samu rauni a cinyarsa wanda hakan ya sa ba zai bugawa kasar ba.
Hatsarin Mota: Mutum 11 Sun Kone Kurmus A Hanyar Zariya Zuwa Kano
Da yake sanar da hukuncin ranar cikarsa shekaru 35 da haihuwa. ya rubuta, “Na yi ƙoƙari da kurakuran da aka yi don zama inda nake a yau kuma ina alfahari da shi! Na rubuta labarina kuma namu yana ƙarewa”.
Benzema ya fara buga wasansa na farko a duniya a 2007 a Les Bleus inda ya zura kwallaye 37 a wasanni 97.
Dan wasan mai shekaru 35 ya kasance ba a cikin hoton tawagar kasar tsawon shekaru biyar bayan da aka same shi da hannu a wani laifin da ya shafi kaset din jima’i da ya girgiza kwallon Faransa.
Kocin Faransa Didier Deschamps ya tuno da shi a shekarar 2021 gabanin gasar cin kofin nahiyar Turai, inda ya zura kwallaye hudu a wasan da aka yi a zagaye na 16.
