Connect with us

News

Jami’an Tsaro Sun Kashe ’Yan Bindiga 5, Sun Cafke 15 A Taraba

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

Hadin guiwar sojoji da ’yan sanda sun hallaka wasu ’yan bindiga biyar da suka addabi Jihar Taraba.

Advertisement

 

Rundunar ta kuma cafke ’yan bindiga 15 a wani samame da ta kai tare da ’yan banga a maboyar ’yan bindiga a dazuka da tsaunikan Kananan Hukumomin Sardaauna da Bali da Gassol na jihar.

Advertisement

’Yan Bindiga Sun Sake Kone Ofishin ’Yan Sanda A Imo

 

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, DSP Usman Abdullahi, ya tabbatar da kashe ’yan bindigar tare da kame wasu 15 a jihar.

Advertisement

 

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa ’yan bindiga sun addabi mazauna wasu yankunan jihar inda suka sace jama’a masu yawan gaske tare da karbar miliyoyi Naira a matsayin kudin fansa.

Advertisement

 

 

Advertisement

’Yan bindigar sun kuma kashe wasu daga cikin wadanda suka sace bayan sun karbi kudaden fansa.

 

Advertisement

Yawan ta’asar da ’yan ta’addan ke tafkawa ne ya sa hukumomin tsaro suka kaddamar ta farmakin, in ji majiyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending