Connect with us

News

Kotu ta ci tarar Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya Naira miliyan 10

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Wata babbar kotu mai zamanta a Awka, babban birnin Jihar Anambra, ta ci tarar Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya Naira miliyan 10 saboda tsare wani dan kasuwa, Chukwuemeka Ekwueme, ba bisa ka’ida ba.

Advertisement

 

Tarar ta shafi Mataimakin Sufeto-Janar, Abutu Yaro, wanda shi ne mai kula da harkokin ‘yan sanda a shiyya ta 13.

Advertisement

 

Gwamnatin Najeriya ta buƙaci NNPC ya rage farashin fetur

Da yake yanke hukunci yayin zaman kotun a ranar Talata, Mai Shari’a D.A. Onyefulu, ya kuma dora wa ‘yan sanda biyan N200,000 ga mai karar a matsayin kudin shari’a.

Advertisement

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya rawaito Alkalin ya ba da umarnin kada ‘yan sanda su yi wa Ekwueme wata barazana ko tsare shi a kan batun da ya yanke hukunci.

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukuncin ya biyo bayan karar da Ekwueme ya shigar kotun mai lamba A/Misc 461/2022 inda ya nemi kotu ta kwato masa ‘yancinsa a wajen ‘yan sanda.

 

Advertisement

Tun da farko, lauyan Ekwueme, Cif Alex Ejesieme (SAN), ya shaida wa kotun cewa ‘yan sanda sun tsare tare da rike wanda yake karewa tsakanin 14 zuwa 28 ga Disamba, 2022 ba tare da sun kai shi kotu ba.

 

Advertisement

Ya ce ‘yan sanda sun tsare Ekwueme ne kan batun da ke da alaka da gini a wani filin da ke kusa da Babban Filin Jirgin Saman Oba da ke yankin Karamar Hukumar Idemili ta Kudu a jihar.

 

Advertisement

(NAN)

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending