Connect with us

News

Ƴan bindiga sun kai wa shugaban kwalejin fasaha Hari

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kwalejin fasaha ta jihar Osun ta tabbatar da harin da wasu ‘yan bindiga suka kai wa shugabanta, Dr Samson Adegoke a jiya Litinin.

 

Advertisement

Kakakin kwalejin, Dr Wale Oyekanmi ne ya bayyana haka a yau Talata a garin Osogbo, inda ya ce an kai wa shugaban makarantar hari ne mintuna 10 da barinsa ofishin da misalin karfe 3:20 na yammacin ranar Litinin.

 

Advertisement

Oyekanmi ya ce maharan sun yi harbi kan motarsa a kusa da unguwar Eti-Ooni bayan yunkurin da suka yi na tare motar ta sa ya ci tura bayan da wata babbar motar dakon yashi ta kawo musu cikas.

 

Advertisement

“An yi sa’a, shugaban kwalejin ko direban sa ba wanda ya samu rauni a lokacin harin. Shugaban kwalejin na cikin koshin lafiya kuma an kai rahoton lamarin ga ƴan sanda,” inji shi.

 

Advertisement

Daily Nigeria ta rawaito Cewa Lokacin da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa ya tuntubi Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Osun, SP Yemisi Opalola, game da lamarin, ya ce ana ci gaba da bincike.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending