Connect with us

News

Yan sanda sun kama mace mai safarar makamai

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar kama wasu mutum biyu masu safarar makamai zuwa jihar ciki har da mace guda.

 

Advertisement

Mutanen biyu – masu suna Emmanuel Emmanuel da wata mace mai suna Nana Ibrahim an kama su ne a kan hanyar Gusau zuwa Wanke zuwa Dansadau – an kama su ne dauke da harsasan bindiga kimanin 325, da mazubin harsasai na ƙirar bindigar AK47 guda ɗaya.

Ƴan bindiga sun kai wa shugaban kwalejin fasaha Hari

Sanarwar ta ce an kama mutanen ne bayan samun bayanan sirri kan mutanen wadanda ake zargin sun ɗaukpo makaman ne daga jihar Benue zuwa wani sansanin ‘yan bindiga a jihar Zamfara.

Advertisement

 

Rundunar ta ce a yayin tuhumarsu mutanen sun amsa laifin cewa sun dade suna gudanar da wannan haramtaccen kasuwanci tsakaninsu da ‘yan fashi a Zamfara da wasu jihohi makwabta.

Advertisement

 

Kwamishin ‘yan sandan jihar Kolo Yusuf ya jaddada burin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da kiran jama’a da su hada hannu da hukumomin tsaro domin tabbatar da ƙudurin rundunar.

Advertisement

 

A ƙarshen makon da ya gabata ma dai rundunar ‘yan sandan jihar ta samu nasarar ƙwace makamai masu yawa a jihar daga hannun masu safarar makaman waɗanda rundunar ta ce sun ɗauko makaman ne daga jihar Taraba domin kai su sansanin ‘yan fashin daji.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending