Connect with us

News

Almundahanar N96bn: Wike Ya Sake Maka  Dan-Amanar Daura Amaechi A Kotu 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnatin na zargin Amaechi da yin sama da fadi sa biliyan 96 lokacin da yake gwamnan jihar.

Advertisement

 

Gwamnatin Ribas ta shigar da sabuwar kara kan tsohon gwamnan jihar kuma tsohon Ministan Sufuri, Dan Amanar Daura Rotimi Amaechi, kan zargin yin sama da fadi da Naira biliyan 96.

Advertisement

 

An maka Amaechi tare da Tonye Cole, dan takarar gwamna na Jam’iyyar APC a jihar bisa zargin sayar da kadarorin jihar.

Advertisement

Ɗan China da ake zargi da kisan Ummita ya ce Naira Miliyan 60 ya kashe mata

Zacchaeus Adangor, babban lauyan Gwamnatin Jihar Ribas, ya tabbatar da shigar da karar.

 

Advertisement

Nyesom Wike, gwamnan Ribas, ya kafa wani kwamitin mutum bakwai don bincikar Amaechi kan zargin cirar Naira biliyan 96 daga asusun gwamnatin jihar a lokacin da yake gwamna.

 

Advertisement

Kwamitin ya kuma binciki batutuwan da suka shafi sayar da kadarorin da tsohon gwamnan ya yi.

 

Advertisement

Kwamitin ya gabatar da rahotonsa a 2015 kan binciken, amma Amaechi ya musanta aikata laifin da ake tuhumar sa.

 

Advertisement

A ranar 27 ga Mayu, 2022, wata babbar kotu ta yi watsi da bukatar Amaechi na hana kwamitin gudanar da bincike a kansa.

 

Advertisement

Sakamakon haka ne, Wike, ya umarci babban lauyan jihar da ya gurfanar da tsohon gwamnan tare da Tonye Cole da wasu mutum biyar da ake zargin na da hannu a badakalar.

 

Advertisement

Wike ya kuma umarci a shigar kan kamfanin Sahara Energy, wanda ake zargin an yi amfani da shi wajen satar kudaden.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending