Connect with us

News

Kada ‘yan Najeriya su ɗaga hankulansu kan ɓarkewar cutar mashaƙo – NCDC

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Shugaban hukumar dakile cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya NCDC ya shaida wa BBC cewa ɓarkewar cutar ‘murar mashaƙo’ ko ‘makarau’ a wasu sassan ƙasar a ‘yan kwanakin nan, ba abu ne da zai ɗaga wa ‘yan ƙasar hankula ba.

Advertisement

 

Kalaman na Dakta Ifedayo Adetifa na zuwa ne bayan da aka samu rahotonnin mutuwar mutum 25 a jihar Kano da ke arewacin ƙasar sakamakon kamuwa da cutar ta ‘murar mashako’ ko ‘maƙarau’, yayin da aka samu rahotonnin mutum 33 da suka kamu da cutar a wasu sasan ƙasar ciki har da birnin Legas.

Advertisement

Ana Zargin ’Yan Sanda Da Bindige Matashi Har Lahira A Zariya

Daga cikin alamomin cutar sun haɗar da zazzaɓi, da bushewar maƙogoro da tari da wahalar numfashi.

 

Advertisement

Waɗanda suka kamu da cutar kan fuskanci zafi a moƙogoronsu a lokacin haɗiyar miyau, da rikiɗewar idanu zuwa launin ja da launin ruwan toka a jikin kakin da suke tofarwa.

 

Advertisement

NCDC ta ce tana lura da mutanen da ake tsammanin sun kamu tare da bayar da shawara ga jama’a da su tabbatar da cewa sun karɓi allurar riga-kafin cutar musamman ƙananan yara.

 

Advertisement

Ana ɗaukar cutar ta hanyar tari da haɗa numfashi da mai ɗauke da ita, ko ta hanyar amfani da wasu abubuwa da mai ɗauke da cutar ya yi amfani da su kamar kofunan shan ruwa ko cokulan cin abinci da tufafi ko kwanciya waje ɗaya da mai ɗauke da cutar.

 

Advertisement

Dakta Adetifa ya ce bai kamata’yan kasar su ɗaga hankalinsu game da ɓarkewar cutar ba, saboda akwai wadatattun magunguna da riga-kafin da za su magance cutar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending