News
Yan bindiga sun sace babban Dan kasuwa a Kano
DAGA ABDULRASHEED MUHAMMAD RABIU
Ƴan Bindiga ɗauke da manya manyan makamai sun kai hari a Garin Kachako na ƙaramar hukumar Takai da ke Kano inda suka ɗauke wani Babban Dan kasuwar garin Alhaji Sabo Mai Goro.
Liberty radio Kano ta rawaito cewa Sai dai matasan garin da mafarauta da jami’an ƴan sanda sun bi sawunsu kasancewar a ƙafa suka gudu da shi suna harbe-harbe.
Bayan kai komo Ƴan Bindigar sun saki ɗan Kasuwar a hanya.
Advertisements
