Sports
Za A Fara Tseren Duniya Na Farko A Najeriya A Watan Afrilu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kwamitin shirya tseren duniya a Najeriya ya sanya ranar Asabar, 9 ga watan Afrilu a matsayin ranar da za a gudanar da zagaye na farko na tseren a Abuja.
Cikin wata sanarwa da daraktan tseren, Olukuyade Thomas ya fitar, ya ce kwamitin ya sanya ranar ce bayan ganawa da masu daukar nauyi da Hukumar Birnin Tarayya, da kuma masu tseren na gida da na kasashen waje.
Kotu ta hana Shugaba Buhari da Gwamnan CBN kara wa’adin amfani da tsoffin kudi
Thomas ya ce rukuni uku za a gudanar a ranar farko, na kilomita 5 da 10 da kuma kilomita 42.195.
Haka kuma akwai al’amuran nishadi da burgewa da dama da za a gudanar yayin tseren.
A baya dai an sanya watan Disambar 2022 ne a matsayin lokacin tseren, sai dai sanarwar da Amurka ta fitar a wancan lokaci cewa ’yan ta‘adda za su far wa kasar ya sa aka dage.
