Connect with us

News

Cutar mashako ta kama mutum 216 ta hallaka 40 a Najeriya

Published

on

 

 

Advertisement

Cibiyar yaki da cututtuka ta najeriya ta tabbatar da cewa mutum 216 ne cutar mashako (diphtheria) ta kama a jihohin Kano da Yobe da Lagos da kuma Osun.

 

Advertisement

Sannan kuma zuwa yanzu kamar yadda bayanan hukumar suka nuna cutar ta kashe mutum 40 a jihohin Kano da Lagos.

Shugaban Tunisia na kama ‘yan jarida da masu hamayya da gwamnatinsa

Daga cikin mutanen da suka rasu Kano tana da 38 yayin da Lagos take da biyu, in ji hukumar.

Advertisement

 

Haka kuma hukumar ta ce mutanen da suka kamu da rashin lafiya wadanda ake ganin ko cutar ce suma ta kama su yanzu sun kai 523 a jihohi biyar.

Advertisement

 

Jihohin kuwa su ne Kano da Yobe da Katsina da Lagos da kuma Osun.

Advertisement

 

Shugaban kwamitin kwararru da ke yaki da cutar ta mashako a hukumar ta NCDC, Dr Bola Lawal, shi ne ya gabatar da wadannan bayanai a wani taro ta intanet a jiya Litinin.

Advertisement

 

Dr Lawal ya ce hukumar ta tashi tsaye wajen taimaka wa kwararrun da ke aikin yaki da cutar a jihohin da ta bayyana na Kano da Katsina da Yobe da Lagos da kuma Osun.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending