News
Boko Haram Ta Hallaka Malaman Makaranta Sama Da 2000 A Shekara 8
Gwamnatin Tarayya ta ce mayakan Boko Haram sun hallaka malaman makarantu 2,295 a jihohin Borno da Yobe da Adama tsakanin shekarar 2009 zuwa 2018, yayin da suka raba sama da dubu 19 da muhallansu.
Kwamandan Rundunar Tsaron (NSCDC), Ahmed Audi ne, ya bayyana haka lokacin da yake kaddamar da wani sabon shirin samar da tsaro a makarantun Nijeriya.
Ranar Masoya: Najeriya ce ta ɗaya a duniya a yawan masu bincike kan soyayya
Audi, ya ce wadannan ‘yan ta’adda sun lalata makarantun da yawansu ya kai 1,500, tare da jikkata dalibai 1,280 tun daga shekarar 2014 kafin a yi nasarar dakile karfinsu.
Kwamandan ya ce wadannan munanan hare-hare sun yi matukar illa a kan harkar koyarwa da kuma ci gaban kasa, abin da ya sa gwamnatin tarayya ta bullo da wannan sabon shiri na samar da tsaron da zai bai wa malamai da dalibai kariyar da suke bukata.
Gwamnatin Tarayya ta dora alhakin samar da tsaro a makarantu a kan rundunar tsaron ‘Civil Defence’ domin ganin an samar da yanayin da ake bukata na bai wa dalibai ilimi.
Shugaban gwamnonin Nijeriya, Aminu Wazirin Tambuwal ya bayyana cewar daukacin jihohi 36 da ke kasar na shirye wajen hada kai da gwamnatin tarayya domin ganin na samu nasarar aikin.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
