Connect with us

News

An baza ƴan sanda a Lagos domin daƙile zanga-zangar ƙarancin Kudi

Published

on

An baza jami’an ƴan sanda a sassan birnin Lagos na Najeriya domin dakile tarzomar da ta ɓarke wadda ake kyautata zaton tana da nasaba da matsalar ƙarancin takardun kudin ƙasar na naira da ake fuskanta.

Rahotanin sun ce wasu manyan bankunan kasuwanci da ke birnin sun ci gaba da kasancewa a rufe.

Advertisement

DA DUMI-DUMI: CBN ya umurci bankunan da su karbi tsofaffin takardun kudi na N500, N1,000

An riƙa jin ƙarar harbe-harben bindiga kuma an toshe manyan hanyoyi da dama inda wasu suka yi amfani da tayoyin da ke ci da wuta.

Ƴan sanda sun ce an dawo da doka da oda a gundumar Mile 12, sannan sun ɗora alhakin tashin hankalin a kan ɓata-gari.

Advertisement

Jama’a na fushi a kan ƙarancin sababbin takardun kuɗin da aka sauya wa fasali, abin da ya haifar da zanga-zanga a farkon makon da ake ciki.

Gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya fito ya roƙi al’umma da su guji yin zanga-zanga a kan canjin kuɗin.

Advertisement

Ya ce gwamnati na yin duk abin da ya kamata domin rage wahalhalun da jama’a ke sha a kan ƙin karɓar tsofaffin kuɗin da kuma ƙarancin man fetur.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending