News
Amurka ta gargaɗi China kan bai wa Rasha tallafi a yakin Ukraine
Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya ce ya gargaɗi China cewa za ta ɗandɗna kuɗarta idan har ta bai wa Rasha wani taimako a yaƙin da take a Ukraine.
Mista Blinken ya bayyana haka ne a wata ganawa da babban jami’in diflomasiyyar China, Wang Yi a wani ɓangare na taron tsaro a Munich.
PDP Ta Nemi Buhari da ya tilasta wa ‘yan APC su Saki Sabbin Kudin Da Su Ka Boye
Da yake magana daga bisani, Mista Blinken ya ce Amurka ta samu bayanai cewa China na duba yiwuwar samar wa Rasha makamai abin da ya ce zai janyo babbar matsala ga alaƙarsu.
Jami’an biyu sun kuma yi magana kan balan-balan ɗin da aka kakkaɓo daga North Carolina a farkon watan nan.
Mista Blinken ya gargaɗi China da kada ta sake ta sake keta sararin samaniyar Amurka yayin da Wang Yi kuma ya ce Amurka ta gurgunta alaƙarsu saboda matakin da ta ɗauka.
-
News5 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
