News
Amurka ta gargaɗi China kan bai wa Rasha tallafi a yakin Ukraine
Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya ce ya gargaɗi China cewa za ta ɗandɗna kuɗarta idan har ta bai wa Rasha wani taimako a yaƙin da take a Ukraine.
Mista Blinken ya bayyana haka ne a wata ganawa da babban jami’in diflomasiyyar China, Wang Yi a wani ɓangare na taron tsaro a Munich.
PDP Ta Nemi Buhari da ya tilasta wa ‘yan APC su Saki Sabbin Kudin Da Su Ka Boye
Da yake magana daga bisani, Mista Blinken ya ce Amurka ta samu bayanai cewa China na duba yiwuwar samar wa Rasha makamai abin da ya ce zai janyo babbar matsala ga alaƙarsu.
Jami’an biyu sun kuma yi magana kan balan-balan ɗin da aka kakkaɓo daga North Carolina a farkon watan nan.
Mista Blinken ya gargaɗi China da kada ta sake ta sake keta sararin samaniyar Amurka yayin da Wang Yi kuma ya ce Amurka ta gurgunta alaƙarsu saboda matakin da ta ɗauka.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
