News
Bayan Ƙorafin da NNPP tayi An Sauyawa Kwamishinan Yan Sandan jahar Kano Wurin Aiki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jim kadan bayan jam’iyyar NNPP ta nemi a cire kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Mamman Dauda bisa zargin nuna bangaranci babban Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Alkali Usman Baba ya sauya masa wurin aiki zuwa jihar Plateau.
A jiya Lahadi ne dai jam’iyyar NNPP tayi barazanar gudanar da zanga zanga a kananan hukumomi 44 bisa yadda tace Kwamishinan Yan Sandan yana nunawa mambobinta.a tsakanin jam,iyya Mai Mulki da mara Mulki banbanci
Sai dai cikin wata takarda da jaridar DAILY NIGERIAN ta samo ta nuna cewa an tura Mamman Dauda zuwa jihar Plateau yayin da aka turo Muhammad Yakubu zuwa Kano.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
