Connect with us

Politics

Atiku ne Ya Tarwatsa Jam’iyyar PDP – Kiyamo

Published

on

Shugaban kwamatin yakin Neman zaban bola tinubu festus keyamo

 

Kakakin kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC,PCC, Festus Keyamo, ya bayyana yadda jam’iyyar PDP ta lalata kanta da kanta.

Advertisement

Keyamo ya ce rashin kishin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya taimaka wajen ruguza jam’iyyar adawar.

Yace Ya lura cewa gazawar PDP na bude tikitin takarar shugaban kasa a 2023 zuwa dukkan sassan kasar “ya ruguza” jam’iyyar.

Advertisement

Bayan haka, Atiku ya fito a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam,iyyar PDP inda ya doke Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas da Gwamna Udom Emmanuel na jihar Akwa Ibom a zaben fidda gwani na shugaban kasa.

Sai dai Keyamo ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa: “Yanzu za a iya cewa gazawar PDP wajen mutunta tsarin shiyya-shiyya na kasa da kuma rashin kishin Atiku, ya lalata PDP cikin sauki.”

Advertisement

Atiku ya sha kaye a hannun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu a zaben shugaban kasa na ranar Asabar da ta gabata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending