Connect with us

News

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamna

Published

on

 

 

Advertisement

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya ta ya Abba Kabir Yusuf murnar lashe zaben gwamnan Kano da yayi.

 

Advertisement

Wannan kunshe cikin wata sanarwa da sakataren yada Labarai na Masarautar Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya fitar ranar Alhamis.

Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam

Sanarwar ta ce al’ummar kasar nan sun karbi tsarin mulkin damokaradiyya da matuqar muhimmacin idan akayi la’akari da yadda suka fito domin jefa kuri’unsu kamar yadda tsarin mulki ya bada dama.

Advertisement

 

Sanawar ta kuma godewa malamai da Limamai da sauran Al’umma bisa addu’ar zaman lafiya da suka dunga yi kafin da kuma bayan gudanar da zaben.

Advertisement

 

Sarkin ya bukaci sabon gwamnan daya hada kai da dukkanin rukunin al’umma wajen tafiyar da gwamnatinsa

Advertisement

 

A cewarsa yin hakan zai taimaka wajen kyautata rayuwar al’umma da kuma kawo cigaban da ake bukata domin bunkasar tattalin arziki ga jihar Kano da kasa baki daya.

Advertisement

 

Alhaji Aminu Ado Bayero yayi fatan dorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano har ma da sauran sassan kasar nan.

Advertisement

 

yayi addu’ar fatan kammala tenure mulkinsa lafiya tareda samun cigaban gwamnatinsa da habaka tattalin arzikin jihar Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending