Connect with us

News

Za A Fuskanci Tsananin Zafin Rana A Wasu Jihohin Najeriya

Published

on

 

 

Advertisement

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a faɗin wasu jihohin ƙasar ƙasar.

Advertisement

 

INEC ta sanya ranar bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni shaidar cin zaɓe

Advertisement

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun ƙunshi Kebbi da Sokoto da Zamfara da Taraba da Adamawa da Oyo da Kwara.

Advertisement

Sai kuma birnin Tarayya Abuja da Nasarawa da Benue da Bauchi da Gombe da kuma Borno.

A cikin wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Lahadi a Abuja, ta ce hukumar ta lura da cewa yanayin zafin rana zai kai maki 40 a ma’aunin celcius a cikin kwanaki biyu masu zuwa.

Advertisement

Nimet ta ce jihohin da makin zai haura 40 sun haɗa da wasu sassan Sokoto da Kebbi da Zamfara da Taraba da kuma Adamawa.

NiMet ta yi gargaɗin cewa jihohi kamar a Bauchi da Gombe da kuma Adamawa na cikin haɗarin rashin jin daɗi musamman a ɓangaren lafiyarsu.

Advertisement

Hukumar ta sharwarci mutane da ke zaune a jihohin da abin zai shafa, da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin.

Ta kuma shawarci masu azumi da kar su riƙa fita cikin ranar, sannan kuma su riƙa shan wadataccen ruwa a lokatan shan ruwa da sahur.

Advertisement

Hukumar ta Nimet ta kuma tabbatar wa mutane cewa za ta ci gaba da bibiyar yanayi don sanar wa al’umma halin da ake ciki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending